8 Oktoba 2024 - 19:18
Gaggawa | Dakin Ayyukan Gwagwarmayar Musulunci: Mujahidanmu Suna Fuskantar Yunkurin Makiya Na Ci Gaba, Inda Suka Sojojin Yahudu Da Suka Wuce 35 Da Jikkata 200.

Hezbollah: A shirye muke mu kai hari a kowane bangare na yankunan da aka mamaye

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul Bait (AS) – ABNA-  ya habarta cewa, dakin gudanarwa na kungiyar Hizbullah a cikin wata sanarwa da ya fitar ya bayyana cewa: Yayin da yake tabbatar da kalaman mataimakin babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Mujahid Naim Qassem dangane da shirye-shiryen dakarun makami mai linzami na kai hari a kan duk wata kafa a cikin kasar Falasdinu da aka mamaye, muna sanar da cewa wannan tsari gwagwarmayar ya dawo daram cikin karfinsa fiye da karfinsa na da.

Dagewar da makiya Isra'ila suka yi wajen kai wa al'ummarmu masu daraja a kasar Lebanon hari zai sa Haifa da garuruwan da ba Haifa ba kamar Kiryat Shmona, Metula da sauran garuruwan da ke kan iyaka da kasar Labanon za su zama hadafin makami mai linzami, wannan shine abin da makiya suka gani a yau a Haifa da kewayenta.

Gwagwarmayar Musulunci tana gani tare da hangen da jin wurin da makiya ba su zato, kuma hannunta na iya kaiwa duk inda ta ga dama a cikin kasar Palastinu da aka mamaye, kuma wutar ba za ta tsaya ga rokoki da jirage masu saukar ungulu masu kai farmaki zuwa cibiyar sahyoniyawan ba.