Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Ministan harkokin wajen kasar Iran ya sanar da shirye-shiryen Jamhuriyar Musulunci ta Iran na bunkasa shirye-shiryen yankin da ya shafi Majalisar Dinkin Duniya kan batun Afganistan.
Husaini Amirabdollahian, ministan harkokin wajen kasar Ira , a wata ganawa da Fereydon Sinirlioglu, babban jami'in MDD na musamman kan tantance al'amuran Afghanistan, yayin da yake nuna jin dadinsa da nadin da aka yi masa a wannan matsayi, ya yi la'akari da muhimmancin da aka samu na Kafa gwamnatin hadaka da yaki da ta'addanci a kasar Afganistan da bukatar tallafawa Ya jaddada shirye-shiryen yankin musamman hakkin makotaka domin taimakawa wajen warware kalubalen Afganistan.
Ya kara da cewa: Afganistan na bukatar mafita cikin gaggawa idan har kasashen duniya ba su mai da hankali sosai kan kalubalen tsaron da wannan kasa ke fuskanta ba sakamakon yunkurin kungiyoyin 'yan ta'adda ba, to munanan sakamakonta zai shafi yankin da ma duniya baki daya.