20 Disamba 2021 - 16:32
Iran: Dakarun IRGC Sun Fara Wani Gagarimin Atisaye A Wannan Litini

Dakarun kare juyin juya halin musulinci na Iran, sun fara wani atisaye na hadin guiwa mai taken manzon Allah karo na 17 a safiyar yau Litini.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - Ana atisayen ne a tekun farisa da mashigar Hormuz da gabar ruwan Hormozgan, Bushehr da lardunan Khuzestan.

Mataimakin babban jami’in gudanarwa na IRGC, kuma mai magana da yawun atisayen Birgediya Janar Abass Nilforoushan ya sanar da fara atisayen na tsawon kwanaki biyar.

Atisayen ya yada dakarun rukunonin dakarun rindinar na sama da kasa dana sararin samaniya da kuma dakarun sa kai na Basij, a wani mataki na dakile barazanar da ake gani daga makiya.

342/