Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{a.s} - ABNA - A wani sako da ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, ta fitar ta ce tana taya Kenya daya daga cikin manyan abokanta a Afrika ta fuskar alakar tattalin arziki murna game da zagayowar wannan rana.
A Yau Lahadi ne al’ummar kasar Kenya ke gudanar da bukukuwan cika shekaru 58 da samun ‘yancin kai daga mulkin Mallaka na turawan Ingila.
Kenya dai ta kasance a karkashin mulkin mallakar kasar Ingila tun daga shekarar 1895 har zuwa ranar 12 ga watan Disamba na 1963.
342/