13 Mayu 2021 - 18:56
​Iran:Araqchi Ya Ce Iran Zata Koma Kan Bada Hadin Kai Da Hukumar IAEA Ne Kawai Idan An Daukewa Kasar Takunkuman Tattalin Arziki

Shugaban tawagar kasar Iran wacce take tattaunawa da jami’an kasashen da suke cikin yarjejeniyar JCPOA, Abbas Araqchi ya ce Iran za ta koma kan bada hadin kai da hukumar IAEA, wacce take sanya ido a kan ayyukan nukliyar kasar ne kawai idan an dagewa kasarsa takunkuman tattalin arzikin da Amurka ta dora mata.

ABNA24 : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Abbas Araqchi ya na fadar haka a yau Laraba a shafinsa na Twitter.

Ya kuma kara da cewa matukar an dauke wa kasar Iran takunkuman tattalin arzikin kafin ranar 21 ga watan Mayun da muke ciki, kamar yadda hukumar ta yiwa kasar alkawari, Iran zata bude kofarta ga hukumar ba tare da wani bata lokacin ba.

Kafin haka dai a ranar 23 ga watan Fabrairun da ya gabata ne kasar Iran ta dakatar da bada hadin kai ga hukumar ta IAEA saboda dokar da majalisar dokokin kasar ta kafa, na dakatar da hadin kan, sai zuwa lokacinda Amurka za ta daukewa kasar takunkuman tattalin arzikin.

342/