9 Maris 2021 - 12:09
Najeriya:An Fara Rarraba Alluran Riga Kafin Cutar Korona Ga Jihohin Kasar

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan fara rabon alluran riga kafin Cutar Korona na Oxfod-Astra Zeneca zuwa jihohin kasar. Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto Faisal Shuaib darectan hukuma bunkasa harkokin kiwon lafiya na farko wato (NPHCDA) ta kasa ne ya bada wannan sanarwan a jiya Litinin.

ABNA24 : Shuaib ya kara da cewa an kammala dukkan shirye shirye a duk fadin kasar don ganin an fara amfani da alluran a dukkan jihohin kasar bisa tsarin da gwamnati ta bayar.

Da farko dai za’a fara yiwa jami’an kiwon lafiya ne da kuma wadanda suke aiki tare da su sannan tsoffin mutane da sauransu.

A ranar jumma’an da ta gabata ce aka fara yin alluran riga kafin cutar Korona a tarayyar Najeriya inda shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Farfesa Yemi Osingbajo suka fara karban alluran a bainal jama’a.

342/