(ABNA24.com) Trump, ya bayyana a taron manema labarai daga fadar White House cewa, zamu fusknaci makwanni biyu masu matukar wahala.
Kalamman na Trump, na zuwa ne a daidai lokacin da adadin mamata da masu kamuwa da cutar coronavirus ke ci gaba da karuwa a kasar.
A alkalumman baya baya nan da aka fitar mutum 865 ne suka rasa rayukansu sanadin cutar, wanda kuma shi ne adadi mafi yawa da aka samu a kasar kawo yanzu tun bayan bullatar.
A Amurka dai Trump, na ci gaba da shan suka akan yadda tunda farko ya yi wa al’amarin cutar ta coronavirus rikon sakainar kashi.
342