Sakamakon dai ya nuna ANC ta samu kasa da kashi 60 na kuri’un da aka kada, duk kuwa da matsayinta na wadda ta jagoranci kasar tun bayan juyi-juya halin 1994 da ya kawo karshen tasirin farar fata a kasar karkashin jagorancin Nelson Mandela.
Sai dai duk da hakan ANC ta samu isasshen kujeru a majalisa da za su bai wa shugaba Cyril Ramaphosa damar ci gaba da jagoranci kasar har zuwa nan da shekaru 5 masu zuwa.