Sanarwar da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan kasar Jimoh Moshood ya aike wa manema labarai ta babban sufeton 'yan sandan kasar Ibrahim Idris, ya ce zai dauki dukkan matakan da suka dace domin ganin zaben ya gudana ba tare da tashin hankali ba.
"Muna bai wa dukkan jam'iyyu umarni da su yi biyaya ga dokokin zabe. Su tabbatar sun gargadi masu yin takara a karkashinsu da masu goyon bayansu da kada su tayar da tarzoma" idan ba haka ba za su dandana kudarsu.