Dakarun kiyaye zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika dake Somaliya (AMISOM), wadanda ke samun tallafin dakarun kasar Somalia, sun cafke wasu mutane biyu da suka kware wajen hadawa kungiyar Al-Shabaab bama bamai a kudancin kasar.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke shirye shiryen karbar bakuncin taron koli na kasashen shiyyar gabashin Afrika, wanda za'a gudanar a gobe Talata.
Dakarun na hadin gwiwa sun ce, sun samu nasarar damke masana hada boma boman ne a lokacin da suke ci gaba da yin sintiri a yankin Lower Juba, dake kudancin birnin Kismayo..
Tuni dai aka girke jami'an tsaro masu yawan gaske a fadin kasar, musamman babban birnin kasar Mogadishu domin tabbatar da tsaro, domin kaucewa duk wata barazana da zata iya kunno kai a yayin taron mai cike da mahimmaci.
............
300