23 Mayu 2016 - 10:36
Buhari Ya Janye Ziyarar Aiki A Lagus

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya dage ziyarar kwanaki biyu da ya shirya kawowa jihar Legas a wannan Litinin.

Mai magana da yawun Buhari, Malam Garba Shehu ya ce, an dage ziyarar har nan da bayan azumin watan Ramadan da ake sa ran farawa a cikin wata mai zuwa.

A halin yanzu Buhari na kan fuskantar ayyuka daban daban da lokutansu ke karo da juna, abinda Garba Shehu ya bayyana a matsayin abu mai wahala ga shugaban.

An dai shirya ziyarar ce domin Buhari ya kaddamar da wasu ayyuka da aka kammala a jihar ta Legas amma dai mataimakinsa, Yemi Osinbajo zai wakilce shi a wani yanayi da ba zai dauki hankulan jama’a ba.

Osinbajo zai kaddamar da kananan ayyukan na Legas amma sauran zai bar wa Buhari har zuwa bayan azumin Ramadan.288