12 Janairu 2015 - 14:04
Ban Ki-Moon ya yi tur da harin Baga

Sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-Moon ya yi Allah-wadai da hare-haren da 'yan Boko Haram suka kai garin Baga da ke jihar Borno a Nigeria

Sai dai har yanzu shugaban Nigeria Goodluck Jonathan bai ce uffan ba game da hare-haren duk da yake daruruwan mutane sun mutu.

Wata sanarwa da ofishinsa ta fitar, Mr Ban ya ce ya yi matukar kaduwar da jin labarin hare-haren, wadanda suka yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Ya bayyana hare-haren a matsayin na ta'addanci.

Mr Ban ya ce a shirye yake ya hada gwiwa da hukumonin Nigeria domin taimakawa mutanen da lamarin ya shafa.ABNA