Umar Khan ya rasu ne a wata babbar asibitin Saliyo da misalin karfe biyu na rana a jiya Talata.
Kafin kamuwa da cutar, Likitan shi ke jagorantar aikin warkar da cutar Ebola a wata asibitin garin Kenama da ke gabas da birnin Freetown.
Alkalumman lafiya a kasar Saliyo sun ce kimanin mutane 489 suka kamu da cutar Ebola a kasar Saliyo, yayin da 159 suka mutu. ABNA