Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: A cikin wata sanarwa, kungiyar ta ce kusan mutane 795,000 da suka rasa matsugunansu a yankunan da ke da tarkace, inda iyalai ke zaune a wuraren da ba su da aminci, suna fuskantar barazanar ambaliyar ruwa.
Hukumar IOM ta jaddada cewa an jinkirta shigar da muhimman kayan da za a iya amfani da su don karfafa matsugunansu, ciki har da itace, plywood, jakunkunan yashi da famfunan ruwa, zuwa Gaza saboda takunkumin da isra’ila ke ci gaba da sanyawa.
Your Comment