27 Yuli 2025 - 11:54
Source: ABNA24
Yamen: Dakarun Yaman Sun Kai Hari Da Makami Mai Linzami Kan Birnin Beersheba Kudancin Isra'ila

Bayan harin makami mai linzami da sojojin Yaman suka kai kan birnin Beersheba da wasu garuruwan Isra'ila, sojojin Isra'ila sun yi ikirarin kakkabo wani makami mai linzami.

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlulbayt (AS) - ABNA – ya habarta cewa: Dakarun kasar Yemen sun sanar da cewa sun kai wani samame na musamman ta hanyar harba makami mai linzami a birnin "Beer-Saba" da ke kudancin Isra'ila.

Yahya Saree, kakakin rundunar sojin Yaman ya kuma sanar da cewa, kungiyar ta kai hari kan muhimman wurare a garuruwan "Eilat", "Ashkelon" da "Al-Khudeira" da jirage marasa matuka guda uku.

Ya yi gargadin cewa, ana la'akari da wasu hanyoyin da za a iya kara kai hare-hare, kuma ana daukar wadannan matakan ne a matsayin martani ga ci gaba da ta'addanci, da yaki da yunwa da kisan kare dangi a Gaza.

A gefe guda kuma Sojojin kasar Isra’ila sun sanar da dakile wani makami mai linzami da aka harba daga kasar Yemen. A halin da ake ciki kuma, na'urorin gargadi na sojojin Isra'ila sun yi ta kararrawa a yankunan gabar yamma da kogin Jordan, da hamadar Negev da kuma kewayen Tekun Mutuwa.

A baya dai sojojin na Isra'ila sun ce sun gano wani makami mai linzami da aka harba daga kasar Yaman kuma suna kokarin kakkaboshi. A lokaci guda kuma, an buga hotuna a shafukan sada zumunta da ke nuna karar fashewar wasu abubuwa da suka ce karar hare-haren na’urar tsaron Isra'ila ne suka haddasa.

Wadannan hare-haren dai na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun kasar Yemen suka kara kai hare-haren makami mai linzami da jiragen sama a kan yankunan Isra'ila da suka hada da filin jirgin sama na Ben-Gurion da tashar jiragen ruwa na Eilat a cikin 'yan makonnin nan.

...................................

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha