8 Satumba 2025 - 13:43
Source: ABNA24
Isra'ila Ta Rushe Gine-Gine 50 A Gaza A Rana Daya

Sojojin Isra'ila na ci gaba da kai munanan hare-hare a yankunan Gaza, sun lalata gine-gine da dama a yankin tare da kashe Falasdinawa da dama da suka hada da kananan yara.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: a ranar Lahadin da ta gabata, kungiyar agaji ta Gaza ta sanar da cewa, sama da gine-gine 50 ne suka rushe gaba daya a hare-haren da Isra’ilan ta kai, kana wasu gine-gine kusan 100 sun lalace, wadanda suka hada da hasumiyai da manyan gine-gine, makarantu, kulab din wasanni da masallatai.

Jami'an kiwon lafiya a zirin Gaza kuma sun ba da rahoton shahadar akalla mutane 21 tun da safiyar yau, ciki har mutane 14 a birnin Gaza.

Sannan Sojoji sun yi wa kauyuka hudu kawanya a arewa maso yammacin birnin Kudus

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha