27 Mayu 2015 - 10:00
An murkushe 'yan bindiga a Kabul

Jami’an tsaron kasar Afghanistan sun yi nasarar murkushe wasu ‘yan bindiga da suka kai hari a kan wani hotel da bakin ‘yan asalin kasashen ketare ke zaune a birnin Kabul, bayan share tsawon awanni ana artabu tsakanin maharan da kuma jami’an tsaro.

Alkalumman da hukumomin tsaro suka fitar na nuni da cewa an kashe ‘yan bindiga 4, yayin da kungiyar Taliban ta fito fili ta dauki alhakin kai harin.

Maharan sun kai harin ne a yankin Wazir Akbar Khan inda mafi yawanci ‘Yan kasashen ketare ka zama a Kabul.ABNA