11 Oktoba 2024 - 13:59
Hizbullah Ta Samar Da Sabon Ɗakin Ayyukan Bada Umarnin Soji  Mai Cikakken Sirri

Kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon tana ci gaba da shirinta na yin yaki na dogon lokaci da gwamnatin sahyoniyawa.

Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) - ABNA - ya habarta maku cewa: Daya daga cikin kwamandojin kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya sanar da cewa, wannan yunkuri na kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon yana shirye-shiryen yin yaki na tsawon lokaci mai tsawo da gwamnatin sahyoniyawa ta hanyar samar da sabbin kwamandojin sojojinta.

 

A wata hira da kamfanin dillancin labaran Reuters, wannan kwamandan ya jaddada cewa mayakan Hizbullah sun kafa sabon dakin ayyukan soji na wannan yunkuri bayan shafe sa'o'i 72 na shahadantar da Sayyid Hasan Nasrallah.


A cewar wannan kwamandan na Hizbullah, sabuwar cibiyar bayar da umarni na ci gaba da aiki duk da hare-haren da Isra'ila ke kaiwa a baya, kuma sabuwar rundunar ta Hizbullah tana aiki ne cikin tsattsar ingantaccen sirri.


Ya yi nuni da cewa: Mayakan kungiyar Hizbullah suna harba makamai masu linzami da yin yaki ne bisa umarnin da jagorancin rundunar ta bayar. Har yanzu kungiyar Hizbullah tana da manyan makamai da suka hada da makamai masu linzami na gaske.


Idan dai ba a manta ba a yammacin ranar Juma'a 27 ga watan September 2024 ne gwamnatin sahyoniyawan ta kashe babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Sayyid Hasan Nasrallah ta hanyar kai hari a unguwar Hara Harik da ke yankin kudancin birnin Beirut babban birnin kasar Labanon da bama-bamai da gine-gine da dama. Har ila yau, a safiyar ranar Talata 01 ga watan Oktoban shekarar 2024, sojojin Isra'ila sun sanar da fara kai farmaki ta kasa a kudancin kasar Lebanon, kan dakarun kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon.