12 Afirilu 2022 - 17:50
Kungiyar Tarayyar Turai Za Ta Rika Sayan Iskar Gas Daga Najeriya Don Rage Dogaro Da Rasha

A jiya Litinin Jami’an Diplomasiyyar kungiyar Turai suka kai ziyara Najeriya inda suka gana da shugaban kamfanin mai na kasa mai mala buni inda ya tabbatarwa da wakilin Turai cewa kamfanin a shirye yake ya kara yawan Iskar gas din da yake fitarwa a kasuwannin duniya,

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Najeriya ce kasa ta 4 dake fitar da iskar gas zuwa Turai inda aka kiyasrta cewa kasha 40 cikin 100 na iskar Gas din da kasar ke fitarwa ana kai shi ne zuwa kasashen Turai.

Tarayyar Turai na son dakatar sayen iskar Gas ne daga Rasha a matsayin mayar da martani kan yakin da ta kaddamar a kan kasar Ukrain, kungiyar tarayyar Turai tana kokarin karfafa dangantaka da Najeriya ne domin samun Karin wuraren da za ta rika sayan iskar Gas da nufin rage dogaro da kasar Rasha

Hukumomin Najeriya sun ce Kasar ta Tabbatar tana da Iskar Gas da ta kai yawan Cubic tiriliyan 209.5 a watan janerun shekara ta 2022 da muke ciki

Daga karshe jakadan kungiyar taryyar Turai a Najeriya Samuel Isopi ya fadi cewa ba suna so mu tsaya a matsayin babbar abokiyar huldar Najeriya ba muna so mu kulla hulda a bangaren sayan isakar gasa saboda mafi yawancin kamfanonin da ake aiki da su na kasashen turai ne.

342/