25 Faburairu 2022 - 20:08
Mutane 6 Sun Rasa Ransu A Sanadiyyar Harin Makamai Masu Linzami Da HKI Ta Kai A Kusa Da Birnin Damascuss

Rahotnnin da suke fitowa daga kasar ta Syria sun ambaci cewa; Jiragen yakin HKI sun kai hari da makamai masu linzami a jiya Alhams, inda su ka kashe mutane shida.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Sojojin HKI sun kai harin ne dai akan wani wuri dake kusa da filin jirgin saman birnin Damascuss.

Sai dai makaman tsaro sararin samaniyar kasar Syria sun kakkabo wasu daga cikin makamai masu linzami da sojojin HKI su ka harba.

Wannan dai shi ne karo na 4 da sojojin HKI su ka kai hari a cikin kasar Syria a wannan watan na Febrairu.

342/