17 Janairu 2022 - 14:41
Tsohon Shugaban Mali Bubakar Kaita Ya Rasu A Yau Lahadi A Birnin Bamako

Rahotanni masu sosa rai da suka fito daga kasar Mali sun bayyana cewa tsohon shugaban kasar Ibrahim Bubakar Kaita da sojoji suka hambarar da gwamnatinsa a shekara ta 2020 ya rasu a yau lahadi a gidansa dake birnin Bamako .

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Iyalan mamacin sun fadi cewa tsaohon shugaban kasar ta mali Ibrahim bubakar kaita da ya jagoranci kasar daga shekara ta 2013 zuwa 2020 ya mutu ne da misalinin karfe 9 na safe agogon mali a gidansa dake birnin Bamako fadar mulkin kasar,

An zabi Ibrahim bubkar kaita ne a shekara ta 2013 kuma sojojin sun kifar da gwamnatinsa ne a watan Agustan shekara ta 2020.

Wannna sanarwar ta zo ne adaidai lokacin da fira ministan kasar ya sanar da cewa za su shigar da kokensu a hukumance na kalubalantar takunkumin da kungiyar bunkasa tattalin arzikin yammacin Afrika Ecowas da kuma kungiyar kula da kudade ta yammacin afirka ta kakaba mata.

342/