Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Wannan yana zuwa ne bayan da shugaban kasar ta masar Abdul Fatah Al-sisi ya bukaci da sanya tare da damawa da mata cikin cibiyoyin shari’a dake jihohin kasar wanda yazuwa yanzu babu mata a cikinsu.
Wasu daga cikin alkalan sun nuna farincikinsu na ganin mafarkin da suka dade suna yi ya zama gaskiya na ganin an shigar da mata cikin cibiyoyin shari’a a kasar,
Matakin da Alsisi ya dauka a watan maris yazo ne bayan da kungiyoyin kare hakkin mata a kasar suka yi kira ga shugaban kasar da cewa lokaci yayi da za’a rike damawa da mata a cikin harkokin siyasa da na shari’a a fadin kasar.
342/