4 Maris 2021 - 08:37
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Isar Da Sakon Ta'aziyyar Rasuwar Sheikh Ahmad Zain Na Kasar Lebanon

A cikin sakon ta’aziyyar da ministan harkokin wajen na Iran ya aike ga kungiyar malaman addinin musulumi ta kasar Lebanon, ya bayyana malamin da cewa ya taka rawa matuka a fagen samar da hadin kan al’ummar musulmi, sunna da shi’a a lokacin da yake raye, ba a cikin Lebanon ba kadai, hadda duniyar musulmi baki daya.

ABNA24 : Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya yaba da matsayar marigayin a fagen gwagwarmaya da ‘yan sahayoniya da jajurcewarsa a kan wajabcin ‘yanto da Palasdinu.

Gabanin rasuwarsa, Sheikh Ahmad Zain ya kasance daya daga cikin fitattun malaman Ahlussunah a Lebanon, kuma ya taba zama alkali a garin Saidha, sannan kuma shugaban majalisar malaman addinin musulunci a kasar.

342/