ABNA24: Bugu da kari an yi kone-konen gidajen a kauyen da shagunan kasuwanci.
Wannan dai shi ne fada karo na biyu na kabilanci a cikin yankin na Darfur a kwanaki kadan.
Fira ministan kasar Sudan Abdullah Hamduk ya sanar da cewa; Daga nan zuwa Alhamis za a aike da jami’an tsaro zuwa yankin domin tabbatar da tsaro ga mutane da bayar da kariya ga gonaki.
Yankin Darfur ya fuskanci matsanancin rikici a 2003 inda aka yi kiyasin kashe mutanen da su ka haura 300,000, da kuma wasu miliyan biyu da rabi da aka raba da matsugunansu.
342/