(ABNA24.com) Shugaban na kasar Iran ya ci gaba da cewa; Tabbas Iran tana gab da samun nasara a yakin na tattalin arziki da Amurka ta shelanta a kanta.
Shugaban na kasar Iran dai ya bayyana hakan ne a yayin taron majalisar koli ta tattalin arzikin kasa wacce ta kunshi banagrori uku na gwamnati da aka kafa bisa umarnin jagoran juyi Imam Khamnei domin magance matsalolin tattalin arziki.
An kafa majalisar ne dai bayan ficewar Amurka daga yarjejeniyar Nukilya da kuma kakaba wa Iran takunkumai.
342/