24 Janairu 2020 - 10:08
Akwai Yi Yiwar Bude Tattaunawa Tsakani Tehran Da Riyad

Ministan harkokin wajen Pakistan Sha Mahmud Quraishi ya bayyana hakan ne a wani taron manema labaru da ya gabatar a birnin Islamabad domin yi wa manema labarai bayani akan ziyarar bayan nan da ya kawo Iran da Riyadh da Amurka.

ABNA24- ta rawaito Quraishi  ba ce wa; Abin da Pakistan ne take son gani a bude tattaunawa a tsakanin Iran da Saudiyya domin warware rashin fahimtar juna da ke tsakaninsu.

Ministan harkokin wajen kasar ta Pakistan ya kuma bayyana yadda kasarsa take da kyakkyawar alaka a tsakaninta da kasashen Iran da Saudiyya, sannan ya kara da cewa; Bude wani sabon rikici a cikin wannan yankin ba abu ne da zai yi kyau ba, kuma muna son ganin zaman lafiya da ci gaba sun sake dawowa a cikin yankin.

A ranar Larabar da ta gabata ne dai minstan harkokin wajen Saudiyya Faisal Bin Farhan ya bayyana cewa kasarsa a shirye take ta bude tattaunawa da Iran.