Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Jummaʼa

27 Disamba 2024

19:12:31
1517434

Jiragen Saman Amurka Sun Kai Hari A Sana'a, Babban Birnin Ƙasar Yemen

An jiyo karar fashewar wani abu a birnin Sana'a


Tashar Isra'ila ta 12 ta bada rahoton cewa Amurka ce ta kai harin a Sana'a a daren yau.

Kafar tashar AlHadath ma ta ruwaito cewa Amurka ta sake kai wa filin jirgin saman Sana'a hari a wanda a kwanakin baya ma ta kai masa hari.

Tashar talabijin ta Isra'ila ta Channel 12 ta yi ikirarin cewa: Isra'ila za ta ci gaba da kai hare-hare kan kasar Yemen cikin makonni masu zuwa

Ita Majiyar Yaman ta rawaito cewa an ji karar fashewar wasu abubuwa biyo bayan harin da jiragen yakin kasar Amurka suka kai a Sana'a babban birnin kasar.

Majiyoyin yahudawan sahyoniya sun sanar da cewa, harin na baya-bayan nan da aka kai a birnin San'a an kai shi ne ba tare da kasancewar sojojin Isra'ila ba.

Mayakan Amurka da Birtaniya sun yi ruwan bama-bamai ne a wurare da dama a Sana'a, babban birnin kasar Yemen.

Suma Majiyoyin Larabawa sun bayyana cewa, filin jirgin saman Sana'a ne aka kai hare-haren a wannan dare.