Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Litinin

11 Satumba 2023

10:16:44
1392855

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Gana Da Mutanen Sistan Balucistan Da Kurasan Ta Kudu

Ya kamata jami'ai su san kimar wadannan mutane kuma su yi musu hidima Tabbas, a Sistan da Baluchistan, an yi ayyuka da yawa, Baluchistan da kuke gani a yau ba Balochistan na zamanin Tagut ba ne, domin naga yanayin mutane a wancen zamanin mutane ba su da komai.

Dubban mutane daga "Sistan da Baluchistan" da Kudancin Khurasan" sun gana da jagoran juyin juya halin.

Kamfanin dillancin labaran Ahlul-Baiti (AS) - ABNA ya habarta cewa, dubun dubatar al'ummar lardunan "Sistan da Baluchistan" da "Khorasan ta Kudu" sun gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci ta hanyar halartar Husainiyar Imam Khumaini.

Nan wasu Bangaren jawaban Jagoran juyin juya halin Musulunci a wannan taro:

Bayanan da muka samu sun nuna cewa gwamnatin Amurka ta kirkiro wata kungiya mai suna Kungiyar Tabarbarewa a kasar nan; tare da manufar haifar da rikici a kasashe ciki har da Iran; domin tada hankula a kasar da suke ganin za su kawo karshen rikicin.

Ta hanyar tunani da nazari, sun cimma matsaya kan cewa, akwai wuraren rikici da dama a Iran: bambance-bambancen kabilanci, bambance-bambancen addini, da batun jinsi da mata, wadanda ya kamata a tunzura su don haifar da rikici. Wannan shi ne shirin Amurka Karin Maganar Farisawa: Rakumi ya ga tsabar auduga a cikin barcinsa!

Ni dai haduwa da ku masoya abin tunawa ne ga Dukkan mutanen Birjand da Khorasan ta Kudu, da mutanen Sistan da Baluchistan. Na yi fada da gwagwarmaya ta farko da gwamnatin Tagut a Birjand a watan Muharram 1342 wato shekaru sittin da suka gabata. Gamuwa ta biyu kuma ita ce a Zahedan a watan Ramadan na shekara ta 1342.

Sun kamanj a Birjand a ranar Tasu'a. Sun kai ni wurin da ake tsare da ‘yan sanda. Mutanen Birjand sun so su afka wa Shahrbani a ranar Ashura, don su fitar da ni daga wurin. Hangen nesa na marigayi Malam Tahami, wanda fitaccen malami ne a daraja ta farko, bai bari hakan ya faru ba. Ya ce hakan zai haifar da matsala ga ga wani bawan Allah. Mutane da malamai a wannan rana suna tare da wannan yunkuri, ba mu kadai ba ne. Birjand tare da dukkan mutanenta da manyan malamanta sun kasance tare da mu.

A cikin watan Ramadan, a wannan shekarar, na je Zahedan, akwai manyan malamai guda biyu a cikin Zahedan; Malamin Shi'a mai darajar farko shi ne marigayi Malam Kafa'ami, malamin Sunna mai darajar farko shi ne marigayi Maulwi Abdulaziz Molazhi. Nan suka kama ni suka kawo ni Tehran suka kai ni Qazal Qal'eh. Marigayi Kafa'ami ya fito fili ya goyi bayanmu, Marigayi Maulwi Abdul Aziz ya fitar da wani hukunci bisa ga maganarmu.

Wato mataki na farko a fili da ni bawan makaskaci na dauka kenan wajen tunkarar tsarin Tagut shi ne marawa wadannan muhimman cibiyoyi guda biyu baya, wadanda a yau su ne cibiyoyin larduna biyu, tare da mutanensu da malamansu.

Ya kamata jami'ai su san kimar wadannan mutane kuma su yi musu hidima. Tabbas, a Sistan da Baluchistan, an yi ayyuka da yawa, Baluchistan da kuke gani a yau ba Balochistan na zamanin Tagut ba ne, na ga yanayin mutane a wancen zamanin mutane ne da ba su da komai. 

An fara aiki a wannan yanki tun daga ranar farko, a can da kuma a Zabul da sauran yankunan lardin. Har yanzu ana aiki zuwa a yau dole ne waɗannan ayyukan su ci gaba da ƙarfi.

Wannan batu na layin dogo yana da matukar muhimmanci, hada arewa da kudu maso gabashin kasar nan da layin dogo na da matukar muhimmanci ga larduna da lardunan dake tsakanin.

Batun ruwan Zabul yana da matukar muhimmanci. Dole ne a yi dukkan ayyuka na dukkan hanyoyin da za a tabbatar da 'yancin jama'a na ruwa.

Akwai abubuwa da yawa a gabanmu da ya kamata a yi. Da a ce an yanke waɗannan shawarar a farkon 80s, lokacin da na zo Baluchistan, da gwamnatoci sun aiwatar da waɗannan shawarwari, da fuskar lardin ta bambanta a yau. Akwai lalaci da rashin kulawa daga wasu gwamnatoci. Amma Yau Alhamdulillahi sun shagaltu da aiki da kokari. Ina fata da yardar Allah wannan fatan ya tabbata.

A yau, babban canji a duniya yana farawa ko kuma ma ya fara. Yau ce ranar da bai kamata a yi watsi da al'ummomin yankin ba kamar yadda suke a lokacin mulkin mallaka, ko kuma bayan yakin duniya na farko. Menene wannan canji? Manyan dalilan wadannan abubuwa ne da yawa. Da farko dai raunanar ma'abota girman kan duniya. Ƙarfin girman Amurka ya yi rauni kuma yana ƙara rauni. Wani babban dali na wannan juyin shine bullowar sabbin masu karfin yanki da na duniya. Sabbin iko suna kunno kai, ko dai masu iko na yanki ko na duniya.

Ana cigaba da sabunta wannan bayanin nan gaba...