Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Asabar

13 Mayu 2023

13:33:16
1365333

An Kafa Rundunar sojojin Musulunci Ta Duniya A Yammacin Kogin Jordan

Qaani: Muna Tare Da Gwagwarmaya Don Murkushe Isra'ila

Babban kwamandan dakarun na Quds ya ce: "Dukkanmu muna tare da fafutukar tsayin daka na gwagwarmaya domin ruguza Isra'ila gaba dayanta", sannan ya ce: "A yau tare da albarkar shiriyar Jagoran juyin juya halin Musulunci, burin Imamul Aazam ya tabbata na ganin kafa hadin gwiwar sojojin Musulunci na duniya.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, kwamanda Isma'il Qaani, a wajen bukin kaddamar da sahannun Jagoran juyin juya halin Musulunci na juyin juya halin Musulunci na "Littafin Khatun wa kwamanda" da kuma zagayowar karo goma sha hudu na kiyaye jihadi da adabin gwagwarmaya da aka shirya a ofishin kula da ayukka da buga littattafai na Jagoran juyin juya halin Musulunci da kuma dacewar lokacin da ake gudanar da shagulgulan zagayowar ranar kafuwar sojojin Fateemiya na goma a birnin Mashhad a ranar 22 ga watan Urdubihisht inda ya dace da zagayowar shahadar Imam Sadik (AS) A birnin Imam Riza (AS) domin tunawa da manyan shahidan gwagwarmayar gwagwarmayar Fatemiyoun da kwamandansu Abu Hamid, inda yace mun taru ne domin tunawa da wannan matsayi, domin bayyanar da girmamawa ga kimar mutanen Afganistan da shahidan.



Abu Hamid shi ne ya ciri tutar manyan shahidai kuma ya zamo jagan shahidai


Ya ci gaba da cewa Abu Hamid shi ne ma’auni na manyan shahidai kuma kambin shahidai, ya kuma kara da cewa: Bayan nuna sahannun girmamawa na Waliyu amril muslimeen, tawagogin gwagwarmaya dana Fatimiyuun ya zama wani faffadan fage mai hade da tushe da wuraren gwagwarmaya a duk faɗin duniya.


Sardar Qaani ya ci gaba da cewa: A wannan fage akwai mutane masu kima da daraja wadanda suke da abubuwa da yawa a hade, amma babban abin da ya hada su shi ne tsaro. Kimar aikin da jaruman Fateemiya suka yi na da fa'ida, bisa ayar Alkur'ani mai girma da ta bayyana matsayin Mujahidai da cewa shahidan Fatemi'un Muhajirai ne kuma mujahidai a martaba ta biyu, kuma suna da siffa mai ban mamaki mai rubanyuwa.


Fagen Gwagwarmaya Ya Zama Babban Fage


Sardar Qaani ya ci gaba da cewa: ‘Yan gwagwarmaya a yau sun rikide daga cibiya da tsiro zuwa wani faffadan kundila da suka hada tushe da wuraren gwagwarmaya daban-daban a duniya. 

A wannan gwagwarmaya akwai mutane masu kishin kasa, masu ilimi da kima, wadanda suke abubuwan da suka hadasu dayawa, amma babban abin da ya hada su shi ne kare Musulunci da daukakar musulmi, sun hadu atare suna masu kare kansu da wanin su.



Kwamandan dakarun Quds ya ci gaba da cewa: Fahimtar aikin da jarumta da Fatimiyyun suka yi yana da wasu fa'ida idan aka kwatanta da na wasu, bisa la'akari da ayar mai albarka da ke bayyana matsayin Mujahidin da makwafta, shahidan Fatimiyyun su na da matsayin Muhajirai biyu da Mujahidai biyu, da kuma rabanye akan aikinsu kamar shahid Hamid da ke Afganistan Ya kare Musulunci, aka horar da shi, kuma a lokacin da ya ji ana bukatar kasancewarsa a wani bangare na wata kasa kuma dole ne ya kare al’ummar Musulmi, sai ya kafa Fatimiyyub da ‘yan kadan daga cikin mujahidan amma albarkacin wannan suna mai kima na yar gwagwarmaya ta farko wato Sayyida Zahra (a.s) ta sanya albarka a aikinsu sannan dubun dubatar matasa suka zo suka bayyana shirinsu na kare mutuncin mutanen da Amurka ta kai musu hari. kuma sun canza al'adar rayuwa mai daraja zuwa wancan bangare na kasa.



Akwai muhimman hadafofi a cikin samuwar Fatimiyyun


Sardar Qaani ya kara da cewa: girmama Abu Hamid yana nufin girmama al'ummar Afganistan da shahidanta, musamman shahidan Fatimiyyun amma kanben wadannan shahidai shi ne Abu Hamid.


Ya kara da cewa: Akwai hadafofi da suke boye a cikin samuwar Fatimiyyun, wanda maimaita kalmar gwagwarmaya da kowa ke yi a wadannan kwanaki, kalma ce daga Alkur'ani da umarnin Allah ga Annabi, amma kura ta lullube ta wanda da nasarar juyin juya halin Musulunci bisa Jagorancin Imam Khumaini (RA) da kuma Jagorancin juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamene'i wannan kalma mai daraja ta bayyana kuma a yau ba ma abokai ba harma da makiya juyin juya halin Musulunci sun yarda cewa gwagwarmaya tana da tasiri a kowane yaki, amma a yau jami'ai daban-daban na siyasa da na soja a fagagenmu daban-daban sun yarda cewa duk wanda ya yi gwagwarmaya to shine ya ke da nasara a fagen fama. Wanda adacen wadanda ke cewa wanda ya fi kayan aiki da makamai shine ke da nasara .


An Kafa Rundunar sojojin Musulunci Ta Duniya


Kwamandan rundunar Qudus ya ce: Bayan fayyace lafazin gwagwarmaya, wani lamari ne mai girma na Musulunci wanda Imaminmu mai girma ya yi umarni da sanya fata a kansa, ya kuma ce; Idan da a ce an kafa rundunar sojojin Musulunci a duniya, shin akwai wanda zai iya karfin hali wajen yi wa ‘ya’yan Manzon Allah (SAW) irin wannan aiki mummunan aiki? A yau albarkacin jagorancin Jagoran juyin juya halin Musulunci, wannan mafarki na Imam mai girma ya tabbata, kuma an samar da hadin gwiwar sojojin Musulunci a duniya.



Sardar Qaani ya ci gaba da cewa: A halin yanzu dai gwamnatin sahyoniyawan tana aikata laifuka a kasar Falasdinu, to amma a kasar Labanon shugaban masu gwagwarmaya yana cewa: "Idan kuka tozarta Kudus to muna nan," wannan murya bata kareba sai ga wata daga Yamen tana cewa muma muna nan, hakanan kuma ana ta daga murya daga wasu kasashe domin kare Falasdinu.



Jaruman matasan Falasdinawa na gudanar da ayyuka 30 a yammacin gabar kogin Jordan a wadansu raneku.



Yayin da yake bayyana cewa jaruman matasan Palastinu suna gudanar da ayyuka sama da 30 a yammacin gabar kogin Jordan a wasu kwanaki, ya ce: Wadannan su ne abunda kungiyoyin gwagwarmaya da kungiyar hadin kan Musulunci ta duniya ta samar.



Kwamandan dakarun Quds ya bayyana cewa: Domin tallafa wa matasan Palastinu, muna goyon bayan wannan gagarumin jarumtakar da za mu iya, a aikace da kuma magana, kuma muna aiki tare domin ruguza gwamnatin sahyoniyawan.



Sardar Qaani ya ce: tunawa da shahidi Abu Hamid za'a yi shi da kyau ne idan aka ci gaba da wannan tafarki na alfahari. Iyalan shahidi Abu Hamid sun tabbatar da cewa sun mayar da mijin aurensu abokin hadakar gwagwarmaya kuma wannan matar ta yi sadaukarwa mataki-mataki tare da wannan kwamanda.

Ya ce: Tun a baya, ana anbatar da al'ummar Afganistan cikin girmamawa da daukakawa, ina fatan Allah ya taimaki wadannan mutane su gina kasarsu ta hanyar da ta dace.

Bayyana Nassin Babban Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci

A karshen bikin, an gabatar da nassin jagoran juyin juya halin Musulunci, inda aka karrama Malama Maryam Gurbanzadeh marubuciyar littafin da kuma Ummal-Banin Husaini da kyautar kur'ani mai albarka mai albarka dak dauke da shedar gimamawa ta babban jagoran juyin juya halin Musulunci, da zobe mai albarka da tsabar nambobin yabo masu tsada.



Har ila yau, an karrama bada kyautar kur'ani ga 'ya'yan Ummul-Banin Husaini da mijin ​​Maryam Gurbanzadeh.



An bai wa Maryam Ghorbanzadeh kyaututtuka guda biyu a karkashin kulawar Ustan Quds Razawi, wanda ya albarkace su daga haramin Imam Rida (a.s.) da masu yiwa Sayyidina Rida as hidima. Ofishin Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayar da kyautuka ga dukkanin iyalan shahidan Fatimiyyun tare da karrama iyalan shahidai 4 a madadinsu.


.........................


karshen sakon