A jawabin da ya gabatar a taron tattalin arzikin duniya kan Afrika a Abuja, Jonathan ya ce "Na yi imani cewa sace wadannan 'yan mata ka iya zama wani mafari na kawo karshen ta'addanci a
Najeriya."
Ya kuma yaba wa Birtaniya da Amurka da China da Faransa a kan tayin taimakawa wajen kubutar da 'yan mata.
Sace 'yan mata fiye da 200 a Chibok makonni uku da suka gabata, ya harzuka jama'a a fadin duniya.
Kungiyar Boko Haram ta ce ita ce ta sace 'yan matan a ranar 14 ga watan Afrilu.
Abubakar Shekau, shugaban kungiyar ya yi barzanar sayar da 'yan matan a kasuwa.ABNA.