Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Hedkwatar Khatamul-Anbiya ta yi gargadin cewa: Idan aka aiwatar da barazanar Amurka, sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za su yarda da fitar da ko digo ɗaya na man fetur ba, kuma za a kai hari a kan ababen more rayuwa na man fetur, gas, wutar lantarki da tattalin arziki na yankin.
Bisa ga gargadin daren jiya, ana sanar da cewa, mashigar Hurmuz har yanzu a rufe take, kuma idan har akwai yiwuwar wani jirgin ruwa ya wuce ta wannan mashigar, dole ne ya wuce ta hanyar da aka kayyade kuma bisa ga shirye-shiryen da aka sanar a baya.
Idan aka aiwatar da barazanar Amurka, sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za su yarda da fitar da ko digo ɗaya na man fetur ba, kuma za a kai hari a kan ababen more rayuwa na man fetur, gas, wutar lantarki da tattalin arziki na yankin.
Barazanar da yar ta’adda Amurka da sojojin ta'addanta ke yi akai-akai ga wannan ƙasa, ba za su haifar da komai ba face faɗaɗa yaƙi a yankin har ma da wajensa.
…………
Ra'ayinka