7 Yuni 2026 - 09:43
Source: ABNA24
Ɗaliban Fudiyya Sun Shirya Walimar Ghadeer A Garin Karaba + Hotuna

Daliban Fodiyya na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagoranci Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H), da ke garin Karaba, sun gudanar da walimar Idin Ghadeer a muhalli Fudiyya Karaba, a ƙaramar hukumar Kubau jihar Kaduna.

A ranar juma'a 5 ga wata Yuni 2026, ɗaliban Fodiyya na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagoranci Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H), da ke garin Karaba, sun gudanar da walimar Idin Ghadeer a muhalli Fudiyya Karaba, a ƙaramar hukumar Kubau jihar Kaduna.

Bayan buɗe taro da Addu'a, sai aka saurari karatun Alkur'ani mai girma daga bakin Fatima Adam, sai kuma (Quiz) a kan Imam Ali (A.S). Malam Adamu Abubakar ne ya gabatar da jawabi, dangane da batun da ya shafi Ghadeer.

Bayan kammala jawabi anyi addu'a aka sallami kowa.

Rahoto Daga: Al'amin Zakariyya Karaba

Zaria Media Forum

Your Comment

You are replying to: .
captcha