Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Abin da ya ninka wannan barazana ga gwamnatin sahyoniyawa shi ne shigar kungiyoyin yanar gizo masu goyon bayan Jamhuriyar Musulunci a wannan fanni. Rahotanni daga kafafen yada labarai na Isra'ila sun ce, a cikin sa'o'i na farko bayan fara rikicin da ake yi a yanzu, an gano fiye da kungiyoyi 60 masu goyon bayan Iran wadanda ke kai hare-haren DDoS, kutsawa da kuma yunkurin rufe kafafen shafukan yanar gizo.
A yayin wannan yakin, wanda aka kwashe sama da wata guda ana gudanar da shi, akalla rahotanni 4019 ne cibiyar ta samu daga bangarori daban-daban na tattalin arziki da mazaunan sahyoniyawa, wadanda mafi yawansu suna da alaka da hare-haren da suka shafi aikin canja tsarin zamantakewa, sarrafa tunani da hankali, samar da sauye-sauyen hangen mutane, da rushewar cibiyoyin tattalin arziki.
Dangane da rahoton tsaro na yanar gizo na shekara-shekara na Microsoft a bara, gwamnatin Sahayoniyawa ta kasance a matsayi na uku a duniya dangane da irin waɗannan hare-haren a shekarar 2025, wanda ya kai kashi 3.5% na yawan hare-haren yanar gizo na duniya.
Your Comment