27 Oktoba 2025 - 13:38
Source: ABNA24
Lebanon: Mabuɗin Zaman Lafiyar Lebanon Ba Shine Miƙa Wuya Ga Sharuɗɗan Isra’ila Ba

Shugaban ƙungiyar goyon baya ga Gwagwarmaya a majalisar dokokin Lebanon ya ce: "Mabuɗin tsaron Lebanon da kwanciyar hankalinta ba ya dogara ne akan miƙa wuya ga sharuɗɗan abokan gaba ba, sai dai ya dogara ne da a tilasta masa mutunta alƙawarinsa da kuma daina kai hare-harensa ta hanyar da ta dace".

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Mohammad Raad, shugaban ƙungiyar goyon bayan gwagwarmaya, ya ƙi amincewa da duk wani yunƙuri na danganta tsarin sake gina ƙasar da matsin lamba daga waje. Ya jaddada cewa: "Waɗanda suka yi yunƙuri, ta hanyar fakewa da waɗannan hujjoji da kuma iƙirarin cewa gwagwarmaya ita ce sanadin hare-haren abin kunya ne hakan kuma sun yi kuskure sosai".

A cikin jawabin da ya gabatar a ranar tunawa da shahidai na birnin Nabatieh, Mohammad Raad ya ce: "Ainihin dalilin kai hari ga makiya shine kwadayinsu na dankwafar da kasar Lebanon. Waɗanda ke neman cewa gwagarmaya kada ta ba wa makiya wani uzuri ko dai ba su fahimci yanayin kai makiya ba ko kuma suna dogara ne da goyon bayan abokan ƙasashen duniya don kare Lebanon bayan rangwamen da Lenbon ta yi".

Dan majalisar dokokin Lebanon ya ce, "Mabuɗin tsaron Lebanon da kwanciyar hankalinta ba shi a miƙa wuya ga yanayin makiya ba, sai dai yana ga a tilasta masu mutunta alƙawarinsu da kuma daina kai hari ta hanyar da za a iya gani karara".

Ya jaddada buƙatar ƙarfafa haɗin kan ƙasa don fuskantar kwadayin gwamnatin Isra’ila da kuma guje wa siyasar da ke raunana fagen cikin gida.

Mohammad Raad ya ce, "Abin da ke cikin maslahar ƙasar shi ne a sake gina gidaje, harkokin 'yan ƙasa, da duk wani matsin lamba na waje ba tare da alaƙa da juna ba".

Ya jaddada adawarsa ga duk wani dage zaben 'yan majalisar dokoki na Lebanon a matsayin wata bukata ta doka da kuma hakki, yana mai cewa, "Yana cikin muradin makiya su dage zaben tare da wani dalili na boye ba".

Dan majalisar daga bangaren gwagwarmaya ya ce, "Makiya suna neman mamaye kasar da kuma dasa yanke kauna a zukatan mutane masu daraja ta hanyar kai hari da lalata gidaje, kasuwanni, wuraren tarihi, da alamomin birane, amma ba za su taba yin nasara ba, domin Lebanon tana da daidaiton kasa, sojoji, da gwagwarmaya. Za mu ci gaba da zama kasa mai 'yanci, mutunci, da nasara".

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha