Harin makami mai linzami na IRGC a kan Haifa ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.
Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahl-Bait As -Abna- ya habarta cewa: majiyoyin yaren yahudanci sun buga wani rahoto kan hasarar rayuka da barnar da harin makami mai linzami na IRGC ya kai kan Haifa da kewayenta.
A cewar rahoton, harin makami mai linzami da Iran ta kai kan Haifa da kewaye ya yi sanadiyar mutuwar mutane uku tare da jikkata wasu kimanin 20.
Ita ma matatar mai ta Haifa an kai harin makami mai linzami, kuma an ga wata babbar gobara ta tashi a Haifa.
Kafofin yada labaran Isra'ila sun bukaci yahudawan sahyoniya da ke zaune a Haifa da kada su dauki hotunan wuraren da makamin ya fada a cikin birnin.
Your Comment