Cibiyoyin kula da al'amuran fursunonin Falasdinu a yau (Lahadi) sun ba da rahoton faruwar wani aikin danniya mai tsanani a kan fursunonin mata na Falasdinu a kurkukun Al-Damun. Dangane da wannan rahoto, sojojin gwamnatin mamaya, ta hanyar kutsawa sashen mata a tsakiyar daren Juma'a, ta amfani da hayaki mai sa hawaye, duka da wulakanci, sun haifar da shaƙewar numfashi da kuma tsananta yanayin raunin jiki na wasu daga cikinsu. A halin yanzu, mata 94 na Falasdinu, ciki har da mata biyu masu juna biyu da marasa lafiya biyu masu ciwon daji, suna cikin wannan kurkuku.
Ma'aikatar Harkokin Waje ta Hukumar Falasdinu, yayin da take yin Allah wadai da aikin yahudawa na kona masallatai biyu a ƙauyukan "Qasra" (Nablus) da "Kur" (Tulkarm), ta jaddada cewa waɗannan hare-hare suna faruwa ne tare da goyon bayan gwamnatin mamaya na Isra'ila kai tsaye, kuma saboda kariyar da ake bas u na rashin hukunta sun daga hukumar ne yasa suke wuce gon a da iri, kuma ta buƙaci al'ummar duniya ta ɗauki matakai masu tasiri da tilaswa don dakatar da waɗannan ta'addanci.
Hare-haren bama-bamai na gwamnatin yahudawa a kudancin Lebanon ba wai kawai sun takaita ga lalata gidaje da hanyoyi da gonaki ba, har ma sun kai hari ga makabartu.