Sayyid Abdul Malik Badreddin Al-Houthi: Matakin hana zirga-zirgar makiya ta tekun Red Sea, Bab Al-Mandab, Gulf of Aden, da Tekun Arabiya ya fara aiki.
Duk wani jirgin Isra'ila da ya bi ta yankin da aka ayyana hanawa, to kai masa hari, kuma wannan qudiri da ya zama wajibi a aikace a za’a gudanar da shi.
Cikakkun bayanai na ma'aunin sojojin ruwan Yaman wajen fuskantar Sahyuniyawa Kawanya da Kawanya
Majiyoyin labarai na Yaman da ke ishara da cewa hare-haren da sojojin ruwan Yaman suke yi kan jiragen ruwan yahudawan sahyoniya bai takaita kawai a kai musu hari ba, har ma sun hada da nutsar da jiragen cikin ruwa, sun kuma jaddada cewa, mai yiwuwa za a aiwatar da wannan kuduri na Yemen din mataki-mataki, kuma a mataki na biyu, za a haramta zirga-zirgar dukkan jiragen ruwa da ke da alaka da Isra'ila a yankin da suke aikin kai hare-haren a yankin kasar Yemen.
Shin Isra'ila za ta mika wuya ga fuskantar Yemen?
Yayin da aka dawo da dokar hana zirga-zirgar jiragen ruwa da ke da alaka da Isra'ila a cikin tekun Bahar Maliya, Tekun Larabawa, Mashigar Babul-Mandab, da Tekun Aden, kwallon shan kayen ta sake fadawa cikin ragar sahyoniyawan ko dai su zabi tsakanin mika wuya ga bukatun Sana'a ko kuma su maimaita shan kasha kamar na baya.
Kakakin kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ya sanar da cewa: Mun yanke shawarar dawo da haramcin da aka yi wa jiragen ruwan Isra'ila a tekun Bahar Rum, da Tekun Larabawa, da mashigar Babal-Mandab.
Shima Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ya sanar a ranar Juma'ar da ta gabata cewa: Idan Isra'ila ta ci gaba da aiwatar da manufofinta na kashe al'ummar Palasdinu da yunwa, sannan kuma ba ta bari a shigar da kayan agaji zuwa Gaza ba, to za mu dauki wasu matakai masu tsauri.
Yaghi mai sharhi kan al'amuran Isra'ila ya fada cewa: Gwamnatin mamaya za ta dauki barazanar Yemen da muhimmanci, domin idan Ansarullah ta aiwatar da wannan barazana, to hakan na nufin komawa cikin wani yanayi na yaki da bangaren Isra'ila.
Komawar yaki dai na nufin kai hare-hare kai tsaye kan jiragen ruwa da ke zuwa yankin Palastinu da Isra'ila ta mamaye, ta haka ne za a fara wani sabon mataki na shan kayen Isra'ila dangane da barazanar Yemen, kamar yadda aka fuskanta a baya bayan nan a yakin da aka yi da Gaza mai muni.
Manufar siyasar kawanya da sanya shinge da Yaman ta sanya za ta haifar da gagarumin sakamako ga Isra'ila da kuma lissafin Amurka, saboda Washington ba ta son shiga ƙarin yaƙe-yaƙe ko aika da jiragen sama don tunkarar Yemen.
Yunkurin lalubo hanyoyin warware matsalar musayar fursunoni da kuma batun agajin jin kai da ke shiga zirin Gaza na da matukar wahala. Sai dai kuma ya kamata a lura cewa, Amurka na ci gaba da kasancewa tare da Isra'ila tare da goyon bayanta mai karfi, don haka dukkan al'amura na iya yiwuwa, ciki har da yiwuwar sake barkewar wani sabon yaki a yankin a daidai lokacin da Isra'ila ke shirin kai wa Iran hari.
Your Comment