23 Satumba 2024 - 19:55
An Ayyana Dokar Ta Baci A Duk Fadin Kasar Falasdinu Da Aka Mamaye

Majalisar ministocin gwamnatin sahyoniyawan ta sanar da kafa dokar ta baci a yankunan da aka mamaye saboda hare-haren Hizbullah.

Kamfanin Dillancin Labaran Kasa Da Kasa Na Ahlul-Baiti As - ABNA Ya Habarta Cewa: majalisar ministocin gwamnatin yahudawa sahyoniya ta amince da ayyana dokar ta baci na tsawon mako guda a dukkanin yankunan Palastinu da ta mamaye.

Bisa labarin da aka bayar, an bukaci ministocin gwamnatin sahyoniyawan da su amince da ayyana dokar ta-baci a cikin gida a dukkanin yankunan Palastinu da ta mamaye a wani bincike da aka gudanar ta wayar tarho. Bayyana wannan lamari yana ba wa sojojin yahudawan sahyoniya karfi da dama don kakaba takunkumi kan yahudawan sahyuniya a dukkan yankunan da aka mamaye.

An sanar da dokar ta bacin ga hukumomin yankin da kwamandojin soji na gwamnatin sahyoniyawan.

Tun da safiyar yau ne gwamnatin sahyoniyawan ta kashe mutane 274 tare da raunata mutane 1024 tare da kai hare-hare ta sama ba tare da kakkautawa ba a yankuna daban daban na kasar Lebanon. Sakamakon wadannan hare-hare, an tilastawa dubban mazauna yankuna daban-daban na Lebanon barin gidajensu.