A wani bangare na jawabin nasa, Ayatullah Ramazani,
yayin da yake ishara da zaben shugaban kasa da kuma girmama shahidai, ya ce:
Sun share mana hanyar zabe. Wadannan shahidai masu daraja a fagen hidima sun
haifar da amana tsakanin al'umma da jami'ai, kuma duk wanda aka zaba a matsayin
shugaban kasa ya zama dole ya ba da fifiko wajen ci gaban hidima da kasancewa a
fage. Shahid Raisi bai san gajiya ba a hanyar hidima.
Ya kara da cewa: Shahidan hidima su suka sanya ya zamo za mu shaidi yadda halartar dinbin al’umma a wajen zaben ranar 8 ga watan Tir. Ina da tabbacin cewa a wannan lokaci na zaben shugaban kasa, za a sauke hakkin kashi 40% na zaben da ya gabata. Idan har yanayin tsaro na tsarin Jamhuriyar Musulunci yana son karuwa a duniya, muna bukatar mafi girman halartar mutane.
Babban sakataren majalisar duniya ta Ahlul-baiti (AS) ya bayyana cewa: Yana da matukar muhimmanci a gare mu cewa muga an zabi shugaban kasa da kuri'a mai girman yawa ta yadda zai iya magance matsaloli a fagage daban-daban da kuma tsare-tsaren da suka dace a kan haka.
A wani bangare na wannan taron, mambobin kungiyar "Shahid Arman Media Headquarters" sun bayyana ra'ayoyinsu da shawarwarinsu game da isar da sako a shafukan intanet da kuma fagen kasa da kasa.
...................................