Wannan rahoton yana dauke da bidiyoyin da suka hada da lokacin da jagoran juyin juya halin Musulunci ya shiga haramin Imam Khumaini tare da fara gabatar da jawabai na zagayowar ranar cika shekaru 35 da wafatin Imam mai girma jagoran juyin juya halin Musulunci, rahamar Allah a gare shi.
Sannan Jagoran juyin juya halin Musulunci yayi bayani
game da batutuwa da dama da suka hada hangen nesa na Imam Khomaini da kuma
batun Falasdinu da fahimtar da Imam Khumaini yayi dangane da hanyoyi na yanto
Falasdinu da cewa tattaunawa ba zata
kaso mafuta ga yanto Falasdinu ba, ya kuma bayani game da shahidin shugaban
kasar Iran Ayatullahi Sayyid Ibrahim Raisi da abokan tafiyarsa da cewa su sun
kasance shahudan hidimtawa al’umma kuma an kashe su akan hanyar hidimtawa al’umma,
yace bayan shahadar Raisi kowa da kowa yana ta magana akan hidimtawarsa
zuciyata ta konu akan rashinsa, a loakcin rayuwarsa ba iya ko da kalma daya su
fada akansa ba, da kuma batutuwa akan gudanar zaben da ake ciki yanzu, da cewa
gasar a cikin zabuka kyakkyawan halaye sune kan gaba wajen zabar yan takara,
