31 Mayu 2021 - 12:54
Abdulmalik Huthi: Ba Za Mu Yarda Da Hada Batun Agaji Da Siyasa Ko Yaki Ba

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Abdulmalik Huthi wanda ya gana da dan sakon musamman na MDD akan Yamen, Martin Griffiths, inda ya bayyana cewa Yemen ba za ta amince da batun alakanta gudanar da ayyukan agaji da na siaysa da soja ba. Huthi ya kara da cewa; Wajibi ne MDD ta fitar da matsayarta gaba-gadi akan wannan batu, mai makon ta zama mai yi wa siyasar kasashen da suke yaki da Yemen, rakiya.

ABNA24 : Har ila yau Huthi ya shaidawa dan sakon na MDD, cewa; Batun ayyukan agaji su ne mabudin warware dukkanin batutuwan da ake Magana akansu, domin hakan ya shafi rayuwar al’ummar kasar kai tsaye.

A farkon wannan watan ne dai manzon na MDD, ya kai ziyarar aiki zuwa kasashen Saudiyya da Oman, a kokarin gano bakin zaren yadda za a warware matsalar da kasar Yemen din take ciki.

Ziyarar ta Griffth zuwa kasar Yemen tana a karkashin kokarin da ake yi ne na samar da yadda za a tsagaita wutar yaki.

342/