ABNA24 : Ministan tsaron na Iran Birgediya Janar Amir Hatami wanda yake ziyarar aiki a kasar India ya gana da daliban Iran da suke karatu a can, yana mai cewa; Samarin Iran sun tabbatar da kwazonsu a fagage daban-daban na Iran.
Birgediya janar Amir Hatami ya kuma ce; Makami mai linzamin mai sunan; Zul-Jinah’ na daukar tauraron dan’adam dalili ne akan ci gaban ilimi da Iran din take samu.
Wani sashe na jawabin ministan tsaron na Iran ya bayyana cewa; Juyin juya halin musulunci a karkashin jagorancin Imam Khumaini ( R.A) ya cusawa al’ummar Iran dogaro da kansu, da jin cewa za su iya kutsawa cikin duk wani fage na ci gaba.
342/