ABNA24 : Amurka ta sanya takunkumi kan babbar mai gabatar da kara ta kotun ICC Fatou Bensouda, wacce ‘yar asalin kasar Gambia ce, da kuma wani babban jami'in kotun.
A cewar gwamnatin Gambiya, wannan mataki na Amurka mummunan saba doka ne, kuma yunkuri ne na kawo cikas ga muhimman ayyukan kotun ta ICC a musamman yakin da take yi wa masu aikata manyan laifuka a kasa da kasa.
Ita dai Amurka ta dau matakin ne a matsayin mayar da martani game da tuhumar da kotun ta ICC ke yi wa wasu sojojin Amurka na aikata laifukan yaki a Afghanistan.
342/