Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Baiti (AS) na kasa da kasa - ABNA - ya habarta maku cewa: Ministan harkokin wajen na wannan gwamnatin ya bayyana shakku game da zaman lafiyar sabuwar gwamnatin Siriya a yayin wani taron aiki a ma'aikatar harkokin wajen kasar inda ya ce sabbin masu mulkin ƙasar Siriya kungiyar 'yan ta'adda ce ba tabbatacciyar gwamnati ba.
Har ila yau ya ce: "Duniya na magana game da sauya tsarin mulki a Siriya, amma abun ba haka ba ne har sai an zabi sabuwar gwamnati ta hanyar dimokuradiyya wacce kuma za ta mullaki dukkan Siriya".
Ya kara da cewa: gungun 'yan ta'adda ne da suka fara a Idlib sannan suka kwace birnin Damascus da sauran wurare kawai.