26 Yuli 2024 - 18:23
An Gudandar Da Sallar Juma'ar Musulmi A Gaban Kofofin Cibiyar Musulunci Da Aka Rufe Ta Frankfurt + Hotuna

Musulman birnin Frankfurt sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewa da rufe cibiyar Musulunci ta wannan birni. Wanda sSakamakon wannan haramcin, za a rufe masallatai 4 na mabiya Shi'a a Jamus tare da kwace kadarorin cibiyar Musulunci ta Hamburg.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na kasa da kasa na Ahlul Bayt (AS) - ABNA – ya habarta maku cewa: Musulman birnin Frankfurt na kasar Jamus sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da rufe cibiyar muslunci ta birnin Frankfurt da mahukuntan Jamus suka yi, inda suka gudanar da sallar Juma'a a gaban cibiyar Musulunci ta wannan birni.

Tare da rike da allunan masu dauke da rubutu mahalarta taron sun yi Allah wadai da rufe cibiyoyin Musulunci a Hamburg da Frankfurt da kuma Berlin da gwamnatin Jamus ta yi, wanda wani mataki ne na takaita 'yancin addini na musulmi a wannan kasa.

Musulman birnin Hamburg na kasar Jamus sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da rufe cibiyar muslunci ta birnin Hamburg da gwamnatin Jamus ta yi a jiya inda suka gudanar da wani gangami a gaban cibiyar Musulunci ta wannan birni.

Idan dai ba a manta ba a ranar Laraba 24 ga watan Yuli ne kafafen yada labaran Jamus suka bayar da rahoton cewa, jami'an 'yan sandan kasar sun kai hari a cibiyar Islama ta Hamburg da wasu cibiyoyin addinin musulunci da ke da alaka da ita, sannan kuma daga aka ftar da sanarwar cewa an haramta ayyukan wadannan cibiyoyi. A cikin wannan yanayi, ma'aikatar harkokin cikin gidan Jamus ta sanar a cikin wata sanarwa cewa ta haramta ayyukan cibiyar Islama ta Hamburg da cibiyoyinta a biranen Frankfurt, Munich da Berlin saboda bin manufar 'yan kishin Islama. Sakamakon wannan haramcin, za a rufe masallatai 4 na mabiya Shi'a a Jamus tare da kwace kadarorin cibiyar Musulunci ta Hamburg.