Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Asabar

20 Mayu 2023

07:11:01
1367131

Al-Houthi: Kasashen Da Ke Wuce Gona Da Iri Ba Su Da Niyyar Yin Sulhu.

"Muhammed Ali al-Houthi" ya wallafa a shafinsa na twitter cewa: "Maganar shugabannin kungiyar kasashen Larabawa ba ta dace da gaskiya ba, kuma ba ta tabbatar da shugabancin al'ummar Larabawa ba."

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, A ci gaba da abunda ya rubuta ya cewa, da a ce an dauki mataki na hakika, da taron kasashen Larabawa ya fitar da kuma aiwatar da yarjejeniyar da suka hada da wadannan sharuddan: dakatar da kudaden tallafawa mayakan sa kai da kasashen mambobin kungiyar kasashen Larabawa tare da mika duk wani tallafi dafa kasashen Larabawa zuwa bangarorin gwagwarmayar Falasdinu, da kuma dakatar da duk wani Ma'amala da taskace dukiyoyi da duk wani aiki na tattalin arziki tare da kowace membar kasa da ba ta aiwatar da wannan yunkurin ba.