Nayi matukar kaduwa da rasa abin da zan Kare Shugaba buhari, bayan na karanta labarin cewa Shugaban ya amince da fitar da kudi har Naira Bilyon 10bn domin gyara muhallan da aka lalata na 'yan Kabilar Birom da rikicin addini ya shafa a Jihar Plateau.
Sarkin yakin buharin Yaci gaba da cewa An yiwa Fulani Musulmi barna wacce ta ninka ta Birom a Mambilla ta Jihar Taraba, an yiwa Hausawa da Fulani barnar da tafi Wannan a Jihar Zamfara, anyi a Birnin Gwari, anyi a Numan, duk wadancan kashe-kashen Shugaban Kasa bai ware ko dubu biyar ba da niyar a taimaka musu, shin su ba yan Nigeria bane? Ko ba su da hakken a taimake su?
To wallahi Buhari kaji tsoron Allah ka sani cewa Allah zai tambaye ka akan wannan Abin da yake faruwa, domin karara kana nunawa musulmi babbancin Addini, kuma ka nuna rayukan Musulmi ba a bakin komai suke ba.
Don haka a matsayin mu na masoyan Shugaban kasa kuma masu nunawa mutane cewa shi mai gaskiya ne dole mu gayamasa gaskiya, domin ya sani ran Kiristoci bai fi na Musulmi ba.
Daga karshe Sarkin yakin ya cigaba da cewa tsarin dokokin kasarnan baya nuna ban banci, don haka ran kowa dayane a Najeriya.
30 Yuni 2018 - 16:51
News ID: 899840

SHUGABA BUHARI YANA NUNAWA MUSULMUN NAJERIYA BABBANCI~~~ CEWAR ATTAHIRU MUHAMMAD MARNONA SARKIN YAKIN BUHARI: