Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Kafofin watsa labarai na Lebanon sun ba da rahoton ci gaba da keta tsagaita wuta daga bangaren Yahudawa ta hanyar kai harin jirgin mara matuki a garin "Tebnin" a kudancin Lebanon.
Bisa ga rahotanni, jirgin mara matuki na Yahudawan ya kai hari a wani wurin sallah kusa da makabartar garin Tebnin da ke kusa da ginin gwamnatin yankin. Kamfanin dillancin labarai na hukuma na Lebanon ya sanar da cewa a wannan hari mutum ɗaya ya shahada, wasu 11 kuma suka jikkata.
A lokaci guda, wannan kamfanin dillancin labarai ya ba da rahoton cewa sojojin ‘yan mamaya sun ci gaba da zalunci ta hanyar kona dazuzzukan da ke gefen garin "Kafr Shuba." A wani ci gaba, kamfanin dillancin labarai na hukuma na Lebanon ya sanar da cewa kusan iyalai 15 da har yanzu sun saura a garin "Al-Mansouri," bayan barazanar Isra’ila, sun tilasta barin yankin.
Sojojin Isra’ila, duk da yarjejeniya da gwamnatin Lebanon, suna ci gaba da keta tsagaita wuta da kuma mamaye wasu yankuna na ƙasar.
Lebanon da Isra’ila a baya sun sanya hannu kan "Yarjejeniyar Tsari" ta hanyar shiga tsakani na Amurka; yarjejeniyar da manufarta ita ce kawo ƙarshen yaƙi tsakanin tsarin Isra'ila da Hizbullah. Wannan yarjejeniya ta samo asali ne bayan zagaye da yawa na tattaunawa kai tsaye tsakanin ɓangarorin biyu a Washington. A lokaci guda, wannan yarjejeniya ta fuskanci suka. Masu suka sun yi nuni ga rashin fayyace matsayin shari'a na yarjejeniyar da kuma rashin tsarin lokaci na ficewar sojojin Sahyoniyawa.
…………..
Ra'ayinka