14 Yuli 2026 - 16:58
Source: ABNA24
Majalisar Ahlul-Bayt (A.S) A Kenya: Jagora Shahidi Ya Kare Musulunci Da Waɗanda Ake Zalunta Da Gwagwarmaya

Majalisar Ahlul-Bayt (A.S) a Kenya ta gudanar da taron tunawa da jagora shahidi Imam Khamene'i, a cibiyar Imam Ridha (A.S) a birnin Mombasa, tare da halartar wasu malamai da shugabannin addinai da sharifai da muminai daga sassan Kenya, inda mahalarta suka yaba da tafarkinsa wajen kare Musulunci da waɗanda ake zalunta, suna jaddada ci gaba da tafarkinsa wajen taimakon gaskiya da adalci.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Majalisar Ahlul-Bayt (A.S) a Kenya, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Malamai masu isar da sakon Musulunci ta Bilal ta Kenya, ta gudanar da taron tunawa da jagora shahidi Ayatullahil-Uzma Sayyid Ali Husaini Khamene'i, a cibiyar Imam Ridha (A.S) a birnin Mombasa, tare da halartar wasu malamai da shugabannin addinai da sharifai da muminai daga sassan Kenya, inda mahalarta suka yaba da tafarkinsa wajen kare Musulunci da waɗanda ake zalunta, suna jaddada ci gaba da tafarkinsa wajen taimakon gaskiya da adalci.

An fara taron da karatun ayoyi daga Alƙur'ani mai girma, sannan aka yi addu'a da karanta waƙoƙin makoki don tunawa da jagora shahidi da sauran shahidan al'ummar Musulunci, sannan wasu malamai suka yi jawabai da suka tattauna tarihinsa da rawar da ya taka wajen hidimar Musulunci, da ƙarfafa hadin kan al'ummar Musulunci, da kuma fuskantar zalunci da girman kai.

Mahalarta sun jaddada cewa tunanin jagora shahidi da gadonsa za su ci gaba da zama tushen kwazo ga masu 'yanci da masu neman adalci, suna yaba wa hikimarsa, da matsayinsa mai tsayin daka wajen kare masu rauni, da ƙoƙarinsa wajen hidimar addini da makarantar Ahlul-Bayt (A.S).

Sayyid Idrusi, daya daga cikin masu jawabi a wannan taron, ya ce jagora shahidi ya kasance abin koyi na jagoranci mai ƙarfi wanda ya kare Musulunci da gwagwarmaya, kuma ya tsaya tare da waɗanda ake zalunta a sassan duniya, yana mai tabbatar da cewa rayuwarsa ta nuna dabi'un sadaukarwa, jarumtaka da jagorancin Musulunci bisa adalci da daukar nauyi.

Sheikh Ali Samwaja shi ma ya tabbatar da cewa jagora shahidi ya taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa hadin kan al'ummar Musulunci, da yaɗa manufofin juyin juya halin Musulunci, da kuma kiran Musulmai zuwa gwagwarmaya wajen fuskantar zalunci da makiya Musulunci.

An kammala taron da addu'a ga jagora shahidi da sauran shahidan al'ummar Musulunci, tare da jaddada wajabcin ci gabantar da sakonsa wajen hidimar Musulmai da kare waɗanda ake zalunta a duk inda suke.

…………….

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha