4 Yuli 2026 - 18:02
Source: ABNA24
Kwamandan Sojojin Ruwa IRGC: Ɗaukar Fansar Allah Na Gaba Da Tabbata Akan Amurka Da Isra'ila 

A yau, muna jimamin rasuwar wani babban mutum wanda yayi shahada a hannun mafi mugunyar mutane da mafi fasikanci a doron ƙasa; makafin mutane da suka ji tsoron ikonsa na ruhaniya, da ƙarfin fasaharsa, da zurfin tunaninsa, saboda ba su iya jurewa hasken imaninsa da basirarsa ba, suka aikata wannan mummunan laifi. Ya kamata waɗannan 'yan Kurdawan masu girman kai da mabiyansu da aka horar da su su sani cewa da wannan mugun aikin bai iya haifar da cikas a tafarkin gaskiya...

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Bayt (AS) – ABNA – ya ruwaito cewa: Admiral Ali Ozma'i, kwamandan sojojin ruwa na Rundunar Tsaro ta Juyin Juya Halin Musulunci, ya sanar da cewa: "Ni da dukkan jaruman mayaƙan sojojin ruwa na Rundunar Tsaro ta Juyin Juya Hali da masu kare mashigar Hormuz mai dabaru, mun yi alkawari a gaban Allah cewa, tare da bin koyarwar shahidai, za mu ci gaba da tafarkin shugaban al'ummar da ya yi shahada cikin ƙarfi da tsayin daka, kuma muna fata da tabbaci cewa saukar azabar Allah a kan Amurka mai ta'addanci da haramtaccen tsarin sahyoniyya bai zamo da nisa ba, kuma tutar gaskiya za ta ci gaba da kasancewa a tsororuwar daraja da iko a hannun magajinsa mai nagarta mai kare wannan zamani."

Ya kara da cewa: "A yau, ba mu na yin bankwana da shi ba ne, sai dai muna sabunta mubaya'a ga koyarwarsa, da tsayin dakansa, da imaninsa, da kuma tafarkin da ya tashi daga ƙirjinsa zuwa sararin samaniyar gaba mai haske," ya kara da cewa: "Wannan nagartaccen bawa mujahadi a tafarkin Allah, ya sadaukar da rayuwarsa don taimakon gaskiya, da kare mutuncin al'ummar Musulunci, da kuma kare tatacciyar koyarwar Musulunci wanda aka saukar ga Annabi Muhammadu SAW. Cikin imani mai ƙarfi da basira mai zurfi da tsayin daka marar girgiza, ya tsaya tsayin daka wajen fuskantar kafirci da girman kai, kuma ya dawwamar da sunansa a cikin manyan mutanen wannan ƙasa."

Ya kuma ce: "A yau, muna jimamin rasuwar wani babban mutum wanda yayi shahada a hannun mafi mugunyar mutane da mafi fasikanci a doron ƙasa; makafin mutane da suka ji tsoron ikonsa na ruhaniya, da ƙarfin fasaharsa, da zurfin tunaninsa, saboda ba su iya jurewa hasken imaninsa da basirarsa ba, suka aikata wannan mummunan laifi. Ya kamata waɗannan 'yan Kurdawan masu girman kai da mabiyansu da aka horar da su su sani cewa da wannan mugun aikin bai iya haifar da cikas a tafarkin gaskiya ba Kai harma sun wulakanta kansu kuma sun la'anci kansu fiye da da a cikin sahun miyagu na tarihi, a wajen fuskantar adalcin Allah, da kuma wajen fuskantar fushi mai halakarawa da azabar mai tsanani na wannan al'umma."

.......

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha